
Seriake Dickson Sanata dake wakiltar mazabar yammacin jihar Bayelsa ya sauya sheka daga jam’iyar PDP ya zuwa NDC.
Tsohon gwamnan ya sanar da matakin da ya dauka na komawa jam’iyar NDC a wurin wani taron manema labarai a Abuja.
A cikin watan Fabrairu ne hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta yi wa jam’iyar NDC rijista a matsayin jam’iyar siyasa.
Dickson ya soki yan adawa dake komawa jam’iyar APC inda ya ce ba daban rikicin da ya addabi jam’iyar PDP ba to babu inda za shi daga jam’iyar.
A cewarsa “Najeriya ba za ta koma karkashin jam’iya ɗaya ba, ba a tsara ta ta zama karkashin jam’iyar siyasa ɗaya ba.”
Ya ce Najeriya kasa ce mai banbance-banbance ta fannin siyasa, al’adu da kuma ƙabila hakan ya sa take buƙatar shugabanci da zai samar da haɗin kai,tafiya tare da kowa da kuma girmama juna.
Sanatan ya ce ya ki amsa kiran shiga jam’iyar ADC saboda ba shi da tabbaci kan manufar jam’iyyar.

