INEC Ta Sauya Ranakun Gudanar Da Zaben 2027 Saboda Ramadan

Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta sanar da sabbin ranakun gudanar da zabukan 2027 a fadin kasar.

A sabon jadawalin, za a gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki ta kasa ranar 16 ga Janairu, 2027. Haka kuma an sanya ranar 6 ga Fabrairu, 2027 domin zabukan gwamnoni da na majalisun dokokin jihohi.

Tun farko, hukumar ta tsara gudanar da wadannan zabuka ne a ranakun 20 ga Fabrairu da 6 ga Maris, 2027.

Hukumar ta ce sauyin ya biyo bayan soke tsohuwar dokar zabe ta 2022 da kuma kafa sabuwar dokar zabe ta 2026.

More from this stream

Recomended