Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta sanar da sabbin ranakun gudanar da zabukan 2027 a fadin kasar.
A sabon jadawalin, za a gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki ta kasa ranar 16 ga Janairu, 2027. Haka kuma an sanya ranar 6 ga Fabrairu, 2027 domin zabukan gwamnoni da na majalisun dokokin jihohi.
Tun farko, hukumar ta tsara gudanar da wadannan zabuka ne a ranakun 20 ga Fabrairu da 6 ga Maris, 2027.
Hukumar ta ce sauyin ya biyo bayan soke tsohuwar dokar zabe ta 2022 da kuma kafa sabuwar dokar zabe ta 2026.
INEC Ta Sauya Ranakun Gudanar Da Zaben 2027 Saboda Ramadan

