Gwamnan Jihar Sokoto State, Ahmed Aliyu, ya bayar da umarnin a fara biyan ma’aikatan jihar albashin watan Fabrairu nan take, sakamakon ƙaratowar watan azumin Ramadana.
Sanarwar da ke ɗauke da wannan bayani ta fito ne ta hannun Abubakar Bawa, shugaban sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na ofishin gwamnan, a yau Alhamis.
Sanarwar ta ce matakin ya shafi: “ma’aikatan Gwamnatin jiha, ƙananan hukumomi, ma’aikatan hukumar Ilimi ta ƙananan hukumomi, da kuma tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a faɗin jihar”.
Bayanin ya ƙara da cewa za a fara biyan albashin ne daga ranar Juma’a 13 ga watan Fabrairu.
Ana sa ran al’ummar Musulmi na duniya za su fara azumin watan Ramadana a ranar 18 ko 19 ga watan Fabrairun bana.
Gwamnan Sokoto Ya Ba Da Umarnin Biyan Albashi Gabanin Azumin Ramadana

