A ranar Juma’a, wani mutum mai shekaru 43 da haihuwa mai suna Kazeem ya mutu bayan da ya fada cikin rijiyar gida a yankin Ile Alapo, unguwar Edun, da ke birnin Ilorin, jihar Kwara.
Hukumar kashe gobara ta jihar Kwara ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da kakakinta, Hassan Adekunle, ya fitar ranar Asabar. A cewarsa, an samu kiran gaggawa daga wani mai unguwa da misalin ƙarfe 10:29 na safe, yana sanar da cewa wani mutum ya fada cikin rijiya.
Jami’an hukumar sun isa wurin cikin gaggawa, inda suka ciro gawar mutumin daga rijiyar. Sanarwar ta kara da cewa, “Kazeem ya dawo daga sallar Idi ne sai ya fadi cikin rijiyar, bayan an ce ya sha wani sinadari mai narkar da hankali da ake kira ‘Colorado’.”
An mika gawar mamacin ga wani jami’in ‘yan sanda mai suna Inspector Babatunde Amos daga ofishin ‘yan sanda na ‘C’ Division da ke Ilorin, yayin da ake jiran dangin mamacin su bayyana don tantance shi da kuma karbar gawarsa.
Daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, Prince Falade John Olumuyiwa, ya bayyana alhinin sa kan faruwar lamarin. Ya kuma yi kira ga al’umma da su guji shan miyagun kwayoyi, yana mai cewa irin wannan dabi’a tana jefa mutum cikin hadurra da kuma kisa kai.
Wani Mutum Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Rijiya a Ilorin Sakamakon Shaye-shaye
