Ƴanbindiga sun kashe mataimakin shugaban jami’ar UDUS


Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe mataimakin shugaban jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Yusuf Sa’idu.

Jami’ar wadda ta bayyana rasuwar Saidu a wata ‘yar gajeriyar sanarwa da ta fitar a shafinta na Facebook a ranar Litinin, ta ce ‘yan ta’adda sun kai wa marigayin hari tare da kashe shi a kan hanyarsa ta zuwa Kaduna daga jihar Sakkwato. 

Sanarwar ta ce, “Farfesa Yusuf Sa’idu, mataimakin shugaban jami’ar bincike da ci gaba na Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto ya rasu a halin yanzu. 

“’Yan bindiga sun kai masa hari tare da kashe shi a kan hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Jihar Sakkwato.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]