Babu ƙamshin gaskiya a batun fara dauƙar ma’aikatan Immigration

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ce hukumar lura da shige da fice ta Najeriya a yanzu haka bata fara ɗaukar ma’aikata ba inda ta shawarci ƴan Najeriya da suyi watsi da duk wa ni talla da ake haɗawa a soshiyal midiya

Hukumar dake lura da ayyukan hukumomin Civil Defence, Gidajen Gyaran Hali, Hukumar Kashe Gobara da kuma Hukumar Lura Da Shige da Fice ita ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da sakataren hukumar,Jafaru Ahmed ya fitar ranar Asabar.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin hukumar kan tallan da ake yaɗawa a kafafen sadarwar zamani ne cewa ta fara ɗaukar aikin Immigration na shekarar 2024.

Hukumar ta ce wannan aikin wasu ɓata gari ne dake neman zambatar yan Najeriya.

“Sanarwar ɗaukar aikin jabu ce kuma bata fito daga hukumar ba,” a cewar sanarwar.

More from this stream

Recomended