NDLEA ta kama wata da ake zargi da safarar hodar Iblis zuwa Pakistan

Hukumar NDLEA da ke yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi Najriya, ta ce ta cafke wata mata ‘yar kasuwa da ake zargi da da hada kai da wasu ‘yan kasar Pakistan wajen safarar hodar iblis zuwa Lahore, babban birnin Pakistan.

Matar mai suna Okefun Darling Chisom, ta shiga hannun jami’an na NDLEA ne a filin tashi da saukar jirage na Legas da ke kudancin Najeriya.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar dauke da sa hannun Daraktan yada labarai, Femi Babafemi, ta ce an kama Chisom da hodar iblis da nauyinta ya kai kilo 8.

NDLEA ta ce Chisom ta boye hodar iblis din ce a cikin na’urar amsa kuwwa, yayin da take kokarin hawa jirgin kamfanin Qatar Airways zuwa Lahore inda za ta ratsa ta Doha a ranar Asabar 5 ga watan Nuwamba.

Bincike ya nuna cewa matar ta na da alaka da wasu ‘yan Pakistan biyu da suka hada da Asif Muhammad mai shekaru 45 da Hussain Naveed mai shekaru 57

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]