Zan bar Najeriya fiye da yadda na same ta – Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa tana da kudurin ganin ta bar mulkin kasar fiye da yadda ta karbi mulkinta.

Shugaban ya kuma bukaci ‘yan kasar da su yi wa gwamnatinsa adalci a kan irin abubuwan da ta cimma zuwa yanzu, musamman ma alkawuran da ta yi kafin zaben 2015.

Shugaban ya yi wadannan kalamai ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Jema’a, Alhaji Muhammadu Isa II, a Kafanchan, yayin da ya je jihar Kaduna ziyarar kwana biyu domin kaddamar da wasu ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]