Adadin Wadanda Coronavirus Ta Kashe a Najeriya Ya Doshi 600

Hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC a Najeriya ta ce adadin mutanen da suka mutu sanadiyyar cutar coronavirus a kasar ya kai 590.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter a daren jiya Talata.

Alkaluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Litinin ya nuna mutum 573 ne suka mutu.

Hakan na nufin an samu karin mutum 17 kenan a yinin ranar Talata.

Izuwa yanzu jimullar mutanen da suka kamu da cutar a duk fadin kasar ya kai 25,694 inda Lagos ta kasance jihar da ta fi galabaita a yawan masu cutar.

Hukumar ta ce cikin wannan adadi an sallami mutum 9,746.

More from this stream

Recomended