Adadin Wadanda Coronavirus Ta Kashe a Najeriya Ya Doshi 600

Hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC a Najeriya ta ce adadin mutanen da suka mutu sanadiyyar cutar coronavirus a kasar ya kai 590.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter a daren jiya Talata.

Alkaluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Litinin ya nuna mutum 573 ne suka mutu.

Hakan na nufin an samu karin mutum 17 kenan a yinin ranar Talata.

Izuwa yanzu jimullar mutanen da suka kamu da cutar a duk fadin kasar ya kai 25,694 inda Lagos ta kasance jihar da ta fi galabaita a yawan masu cutar.

Hukumar ta ce cikin wannan adadi an sallami mutum 9,746.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...