2019: PDP ta yi martani dangane da dage zaben Najeriya

Shugaban jam’iyar PDP a jihar Adamawa Barr. A.T Shehu, ya bayyana cewa akwai lauje cikin nadi a wannan lamarin ganin yanayin da aka dage baban zaben da aka shirya yi yau asabar.

Shima dan takarar babbar jam’iyar adawa ta PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, yace nan bada jimawa ba, zasu gana da masu ruwa da tsaki don fitar da matsaya, kan dage zabe, amma shi ma ya nuna bacin ransa.

Tuni wasu ma’aikatan wucin gadi da aka dauka don gudanar da aikin zaben suka nuna bacin ransu, musamman wadanda aka tura yankuna masu nisa.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...