Ƴanbindiga sun yi garkuwa da wani mutum mai shekaru 27 a garin Abaji

Wasu ƴan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace,wani mutum mai suna, Kabiru Sani dan shekara 27 mazaunin Anguwar Abbatuwa dake cikin garin Abaji.

Wani mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Yakubu ya ce lamarin yafaru ne 1:20 na dare lokacin da ƴanbindigar suka dirarwa gidan.

Ya ce masu garkuwar sun samu nasarar shiga gidan bayan da suka balla kofar shiga ciki.Inda ya ce bayan da suka gama bincike dakunan gidan ba tare da ganin mahaifin wanda suka yi garkuwa da shi ba ka wai sai suka yi awon gaba da matashin ya zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Ya kara da cewa ƴanbindigar sun gudanar da ta’asar ne ba tare da harba ko bindiga ba domin kada su ja hankalin makota.

Wakilin jaridar Daily Trust ya gano cewa mahaifin matashin da aka yi garkuwa da shi wanda ke sana’ar sayar da shanu da awaki na kokarin tuntubar masu garkuwar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...