Ƴanbindiga sun kashe shugaban jam’iyar APC a jihar Imo

Yan bindiga sun harbe, Mista Ifeanyi Ozoemena,shugaban jam’iyar APC na mazabar Logara/Umuohiagu dake karamar hukumar Ngor Okpala ta jihar Imo.

Wakilin jaridar Daily ya tattara bayanan dake cewa an harbe Ozoemena har lahira ranar Talata da daddare sa’o’i biyu bayan da ya jagoranci taron jam’iyyarsa a mazabarsa a shirye shiryen da suke na tunkarar zaben shugaban dana yan majalisun tarayya.

A cewar wadanda suka sheda abinda ya faru, an harbe shugaban na APC a cikin gidansa lokacin da iyalansa ke tare da shi.

Mataimakin shugaban kungiyar cigaban al’ummr Logara wanda ya tabbatar da faruwar kisan kan da ya bayyana da abu marar dadin ji.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Dasuki Galadanchi ya tabbatar da faruwar lamarin a tattaunawar da ya yi da wakilin jaridar Daily Trust ta wayar tarho inda ya ce tuni jami’an tsaro suka dauke gawar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...