Ƴan sanda Sun Kama Mai Garkuwa Da Mutane A Jihar Taraba

Rundunar yan sandan jihar Taraba ta ce jami’anta sun kama wani mai suna, Aliyu Muhammad akan titin Jalingo-Yola da ake zargin mai garkuwa da mutane.

Joseph Eribo, kwamishinan ƴan sandan jihar shi ne ya bayyana haka ranar Laraba a Jalingo.

Eribo ya ƙara da cewa mutumin da ake zargi ɗan shekara 35 ya fito ne daga karamar hukumar Mubi ƴan sandan kwantar da tarzoma ne suka kama shi a ranar Talata a cikin wata mota ƙirar Toyota mai ɗauke da rijistar namba YLA 321 ZY.

Ya ce jumullar miliyan 8.5 na tsabar kuɗi aka samu a cikin motar sai kuma miliyan 4 a asusunsa na banki, wayoyin hannu guda 7 da katin MTN na 3000 da guraye guda bakwai na daga cikin abubuwan da aka gano a tare da shi.

Ya ƙara da cewa wanda ake zargin ya yi yinkurin bawa jami’an ƴan sanda cin hanci kafin a kama shi.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an ƴan sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...