Ƴan sanda sun kashe mutane uku masu garkuwa da mutane a jihar Katsina

Rundunar ƴan sandan jihar Katsina ta ce wasu mutane uku aka kashe da ake zargin masu garkuwa da mutane ne lokacin da suke ƙoƙarin yin garkuwa da mutane akan hanyar Dustinma zuwa Ƙanƙara.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar na cewa lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 4:30 na yamma.

Aliyu ya ce masu garkuwar da suka tsare hanyar na ɗauke da muggan makamai.

Ya ƙara da cewa jami’an ƴan sanda sun isa wurin akan lokaci inda suka shiga musayar wuta da ƴan bindigar kuma suka kashe ƴan uku nan take.

Masa’udu Saidu jami’i a kungiyar ƴan bijilante ya samu raunin harbin bindiga a hannu kuma yana samun kulawa a asibiti a cewar mai magana da yawun rundunar ƴan sandan.

More News

Zargin badaƙala: Kotu ta hana Hadi Sirika fita ƙasar waje

A ranar Alhamis ne babbar kotun birnin tarayya Abuja ta hana tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika, diyarsa Fatimah da sirikinsa Jalal Hamma...

Kotu ta bayar da belin Hadi Sirika da ƴarsa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da belin tsohon ministan harkokin sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da kuma wasu mutane uku kan...

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...