Ƴan majalisa a Najeriya na neman ƙarin albashi

‘Yan majalisar wakilai na neman a sake duba albashinsu da alawus-alawus, biyo bayan cire tallafin man fetur da kuma halin da tattalin arzikin kasar ke ciki a halin yanzu.

Rahotanni sun nuna cewa an nuna bukatar hakan ne a taron da ‘yan majalisar suka yi a ranar 11 ga watan Yuli bayan sun shiga zaman zartarwa a zaman majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci shugaban majalisar, Tajudeen Abass, dalilin da ya sa aka jinkirta biyansu albashi da alawus-alawus, lamarin da ya sa wasu daga cikinsu ke neman lamuni.

Sai dai daya daga cikin ‘yan majalisar da ya halarci taron amma ya bukaci a sakaya sunansa saboda ba a ba shi damar yin magana kan sakamakon zaman majalisar zartarwa ba, ya ce sun yi maganar karin albashi ne kawai ba tare da jinkiri ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]