Ƴan majalisa a Najeriya na neman ƙarin albashi

‘Yan majalisar wakilai na neman a sake duba albashinsu da alawus-alawus, biyo bayan cire tallafin man fetur da kuma halin da tattalin arzikin kasar ke ciki a halin yanzu.

Rahotanni sun nuna cewa an nuna bukatar hakan ne a taron da ‘yan majalisar suka yi a ranar 11 ga watan Yuli bayan sun shiga zaman zartarwa a zaman majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci shugaban majalisar, Tajudeen Abass, dalilin da ya sa aka jinkirta biyansu albashi da alawus-alawus, lamarin da ya sa wasu daga cikinsu ke neman lamuni.

Sai dai daya daga cikin ‘yan majalisar da ya halarci taron amma ya bukaci a sakaya sunansa saboda ba a ba shi damar yin magana kan sakamakon zaman majalisar zartarwa ba, ya ce sun yi maganar karin albashi ne kawai ba tare da jinkiri ba.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...