Ƴan fashi sun kashe mutane a Neja

Ƴan bindiga sun kashe manoma 25 tare da yin garkuwa da mata da ‘yan mata da dama daga al’ummomi daban-daban a karamar hukumar Rafi ta jihar Neja.

Rahotanni sun ce an kai harin ne da misalin karfe biyu na rana a kauyuka biyar.

Alkaluma sun nuna cewa mutane 13 ne suka rasa rayukansu a yankin Kusherki, an kuma kashe wasu 12 a kauyen Gidigori, yayin da wasu da dama suka rasa rayukansu.

Rahotanni sun nuna cewa ayyukan jin ƙai a yankin ya kara lalacewa ne tun daga ranar Laraba, yayin da daruruwan ‘yan gudun hijira da suka hada da mata da kananan yara daga kauyuka daban-daban suka yi tururuwa zuwa Kagara, hedikwatar karamar hukumar Rafi, inda suka bar kauyukan nasu ga ‘yan fashi.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...