Ƴan bindiga sun kashe manoma 25 tare da yin garkuwa da mata da ‘yan mata da dama daga al’ummomi daban-daban a karamar hukumar Rafi ta jihar Neja.
Rahotanni sun ce an kai harin ne da misalin karfe biyu na rana a kauyuka biyar.
Alkaluma sun nuna cewa mutane 13 ne suka rasa rayukansu a yankin Kusherki, an kuma kashe wasu 12 a kauyen Gidigori, yayin da wasu da dama suka rasa rayukansu.
Rahotanni sun nuna cewa ayyukan jin ƙai a yankin ya kara lalacewa ne tun daga ranar Laraba, yayin da daruruwan ‘yan gudun hijira da suka hada da mata da kananan yara daga kauyuka daban-daban suka yi tururuwa zuwa Kagara, hedikwatar karamar hukumar Rafi, inda suka bar kauyukan nasu ga ‘yan fashi.