Ƴan bindiga sun kashe sojoji biyu da wasu mutane uku a jihar Nasarawa

Ƴan bindiga sun kashe sojoji biyu da kuma wasu mutane uku a yayin da suka ƙona gidaje da dama a Umaisha dake ƙaramar hukumar Toto ta jihar Nasarawa.

Ba wannan ne karon farko ba da ƴan bindiga su ke kai wa jami’an tsaro hari ba a yankin ko da a ranar 7 ga watan Faburairu ƴan bindigar sun kashe sojoji uku da fararen hula biyu a wani harin kwanton ɓauna da suka kai musu a ƙauyen Katakpa dake maƙota da Umaisha.

Har ila yau a ranar 25 ga watan Faburairu ƴan bindigar sun kai farmaki ƙauyen na Katakpa suka kashe baraken gargajiya na garin, Abubakar Ahmadu tare da wasu mutane 11 da kuma ƴan sanda biyu tare da ƙona gidaje ciki har da marigayin.

Da yake tabbatar da harin na baya-bayan nan wani mazaunin Katakpa, Ibrahim Sa’idu ya ce lamarin ya faru ne 02:33 na daren ranar Laraba lokacin da ƴan bindiga suka ƙaddamar da farmaki kan ƙauyen Shege.

“Abin da ya faru sojojin da aka ajiye a Katakpa sun ƙarbi kiran kai ɗaukin gaggawa a yayin da suke kan hanyarsu ne ƴan bindigar su kai musu kwanton ɓauna inda suka kashe sojoji biyu nan take,” ya ce.

Ya ce an kai gawarwakin sojojin babban asibitin Toto inda daga nan aka kai su Cibiyar Kula Da Lafiya ta Tarayya dake Lafiya.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...