Ƴan ƙwadago sun fasa tafiya yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago na NLC da TUC a Najeriya sun dakatar da shirinsu na tafiya yajin aiki nan da wata daya.

Sun bayyana haka ne ranar Litinin da daddare, suna masu cewa gwamnatin tarayya ta kara N35,000 a albashin ma’aikatanta wanda za a soma biya daga watan Satumba.

Kungiyoyin dai sun fara maganar yakin aikin ne dai sanadiyyar wahala da ƴan Najeriya ke sha saboda cire tallafin man fetur da kuma wasu al’amurra.

More from this stream

Recomended