Gwamnatin kasar Amurka ta fara shirin janye dakarunta daga jamhuriyar Nijar kamar yadda kafar yaÉ—a labarai ta CBS ta bada rahoto.
Wani jami’in ma’aikatar wajen Amurka ya faÉ—awa kafar yaÉ—a labaran cewa Kurt Campbell mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka da kuma Ali Lamine Zeine firaministan Æ™asar Nijar sun yi wata ganawa ranar Juma’a a birnin Yamai kan yadda za a shirya ficewar dakarun cikin tsari daga Nijar.
Jami’an biyu sun jaddada muhimmancin dangantaka a tsakanin Æ™asashen biyu inda suka amince su cigaba da haÉ—a kai a fannin da É“ukatar su tazo É—aya.
Ƙasar ta Amurka ta amince ta rufe sansanin sojanta dake garin Agadez inda anan ne ta girke jiragen yaƙinta marasa matuƙi.
Kusan sojan Amurka 1000 ne ke zaune Æ™asar ta Nijar inda suke yaÆ™i da Æ™ungiyoyin Æ´an ta’adda dake yankin Sahel.