Ƴan bindiga sun sace wasu matasa akan hanyarsu ta zuwa sansanin NYSC dake ‌Kebbi

Wasu yan bindiga a Zamfara sun yi garkuwa da wasu matasa da suka kammala jami’a akan hanyarsu ta zuwa sansanin yan yiwa kasa hidima dake jihar Kebbi.

Matasan sun fito ne daga jihar Akwa Ibom.

Eddy Megwa daraktan yaɗa labarai na hukumar ta NYSC dake Abuja shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin.

Megwa ya ce anyi awon gaba da matasan ne da daddare a Zamfara lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa sansanin da aka tura su a jihar Kebbi.

Uku daga cikinsu sun samu nasarar tserewa a lokacin da yan bindigar suka tsare su.

Megwa ya kara da cewa yanzu haka shugaban hukumar ta NYSC yana Zamfara domin lalubo hanyar da za a kuɓutar da su.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...