Ƴan bindiga sun sace tsohon ɗan takarar gwamnan Filato

Rahotanni daga jihar Filato a Najeriya na cewa ƴan bindiga sun sace tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Filato a zaɓen 2019, Nkemi Nicholas Nashe.

Mista Nashe wanda jigo ne a Jam’iyyar PDP, ya taɓa riƙe muƙamin Shugaban Ƙaramar Hukumar Shendam a baya.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa wani makusancin Mista Nshe ɗin na cewa jama’ na zaman ɗar-ɗar tun bayan faruwar wannan lamari a Shendam.

Shi kansa gwamnan jihar mai ci a yanzu Simon Lalong ya fito ne daga Ƙaramar Hukumar Shendam.

Sace Mista Nshe na zuwa ne ƙwanaki kaɗan bayan sakin wani basarake a jihar ta Filato da aka sace, Charles Mato Dakat.

Sai dai sojoji da ke jihar sun bayyana cewa sun kama mutum takwas da suke zargi da hannu a sace basaraken.

More News

Ƴan bindiga sun buɗe wuta kan motar kulob ɗin Sunshine Stars

Ƴan wasa da kuma jagororin kungiya ne suka jikkata a wani hari da ƴan bindiga suka kai kan tawagar kungiyar kwallon kafa ta Sunshine...

Za a hukunta waɗanda ke da alhakin kai harin bam a ƙauyen Kaduna

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya ce wadanda suka kai harin bam da jirage marasa matuka a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi...

Ɗalibai sun yi gagarumar zanga-zanga saboda satar dalibai a Lafia

Daliban Jami’ar Tarayya Lafia (Fulafia) sun fito kan tituna suna nuna rashin amincewa da ci gaba da yin garkuwa da ’yan’uwan da ake yi....

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 tare da lalata sansaninsu 4 a Borno

Sojojin rundunar kasa da kasa dake samar da tsaro a yankin tafkin Chadi sun kashe mayaƙa 6 na ƙungiyar ƴan ta'adda ta ISWAP...