Zamu Maida Martani A Kan Duk Kasar Da Ta Hana ‘Yan Najeriya Biza

VOA Hausa

Shugaban ma’aikatar shige da ficen ta Najeriya Muhammad Babandede ya ce ma’aikatar sa ta shirya tsaf domin yin aiki a kan fasinjoji da zasu sauka a manyan filayen saukar jiragen saman kasar guda biyu da suka hada da na Lagos da na babban birnin tarayya Abuja, a daidai wannan lokaci da jiragen waje suka fara shigowa Najeriya.

A wata hira ta musmman da Muryar Amurka, Babandede ya tabbatar da cewa an dauki kwararan matakan da suka dace game da cutar coronavirus a filayen saukar jiragen saman. Ya ce sun kare ma’aikatan su daga kamuwa da COVID-19.

Ya ce gwamnati ta fitar da sabuwar doka cewa kafin fasinja ya shiga jirgi sai ya yi gwajin cutar kafin ya iso Najeriya kuma duk wanda bai bi wannan doka ba za a hukunta shi, ko wanene koda kuwa dan Najeriya ne kuma haka zai kare ma’aikatan mu da zasu biciki fasfunan fasijojin.

Shugaban ma’aikatar shige da ficen ya ce akwai kuma matakai da ma’aikatar sat a dauka da hadin gwiwar ma’aikatar harkokin cikin gida game da ba ‘yan kasar waje mazauna Najeriya na cikin gida da waje da takardun bizar su ta kare ko kuma zata kare daman gyara takardun su, abinda ya kira sauki da hukumomin Najeriya suka yiwa mutane.

Sai dai ya kara da cewa Najeriya zata maida martani a kan kasar da ta hana ‘yan Najeriya bizar shiga kasarta saboda sabuwar bizar da shugaban kasa ya wallafa ta NVP2020 .

A cewar Muhammad Babandede, manyan filayen saukar jirage biyu kadai ne aka bude domin fara jigilar fasinjojin kasashen waje kuma a hankali za a bude sauran filayen sauka da tashin jiragen saman kasa da kasa a Najeriya.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...