Za a samar da maganin HIV mai ɗanɗanon inibi ga yara a Afirka

Magani

Hukumomin agaji sun ce za a samar da magani mai ɗanɗanon itacen inibi mara tsada ga yaran da suke ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki ta HIV a Afirka a shekara mai zuwa.

Za a samar da maganin ne har ma ga jariran da suke ɗauke da cutar.

Majalisar Dinkin Duniya ta ƙiyasta cewa a cikin yara fiye da miliyan ɗaya da rabi dake ɗauke da ƙwayar cutar a duniya, rabinsu ne kaɗai ke iya samun magani.

Wani abu da ke hana yaran da suke ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki su sha maganin cutar shi ne saboda rashin daɗinsa ga kuma ɗaci.

Kwararru a fannin lafiya sun ce samar da maganin HIV ɗin ga yara mai ɗanɗanon inibin, zai matukar taimakawa yaran su rinƙa sha ba tare da damuwa ba.

A cewar ƙwararru nan da wasu watanni masu zuwa yaran da suke a ƙasashen Benin da Kenya da Malawi da Najeriya da kuma Zimbabwe za su samu irin wannan magani na cutar ta HIV mai dandanon inibi.

Karin bayani

Masana kiwon lafiya dai na kara nanata cewa idan mutum ya kamu da cutar HIV, to ba shi ne karshen rayuwarsa ba, domin akwai maganin da ake sha, wanda idan har mutum ya kiyaye da ka’idar maganin to ba lallai ne idan aka ganshi ace ma yana da cutar ba.

Shirin haɗin gwiwa kan yaƙi da HIV da AIDS na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce ƙiyasin mutum miliyan 38 ne ke fama da ƙwayar cuta mai karya garkuwar jiki a duniya, kuma sama da miliyan 35 ne suka mutu tun fara gano cutar a 1984.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...