Wasu dalibai biyu na kwalejin ilimi ta jihar Kwara dake Ilorin za su fuskanci kwamitin ladabatarwa kan zargin da ake musu na nuna rashin ɗa’a a yayin bikin kammala karatunsu.
Daliban da abun ya shafa sun haɗa da Sulyman Tawakkaltu da Muhammad AbdulSalam dukkansu na sashen karatun aikin noma.
A wani hoto da ya karaɗen kafar sadarwar zamani ya nuna Abdulsalam riƙe da nonon Tawakkaltu a yayin bikin kammala karatunsu.
A cewar wata takarda da makarantar ta fitar za a hukunta daliban ne kan yadda suka nuna rashin ɗa’a.
Makarantar ta umarci kwamitinta na hukunta daliɓai da su ɗauki matakin kan daliban biyu domin ya zama izina ga sauran ɗalibai.