Za a hukunta Abdulsalam da Tawakkaltu kan nuna rashin ɗa’a

Wasu dalibai biyu na kwalejin ilimi ta jihar Kwara dake Ilorin za su fuskanci kwamitin ladabatarwa kan zargin da ake musu na nuna rashin ɗa’a a yayin bikin kammala karatunsu.

Daliban da abun ya shafa sun haɗa da Sulyman Tawakkaltu da Muhammad AbdulSalam dukkansu na sashen karatun aikin noma.

A wani hoto da ya karaɗen kafar sadarwar zamani ya nuna Abdulsalam riƙe da nonon Tawakkaltu a yayin bikin kammala karatunsu.

A cewar wata takarda da makarantar ta fitar za a hukunta daliban ne kan yadda suka nuna rashin ɗa’a.

Makarantar ta umarci kwamitinta na hukunta daliɓai da su ɗauki matakin kan daliban biyu domin ya zama izina ga sauran ɗalibai.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...