Za a bude ofisoshin gwamnati ranar Litinin a Lagos – AREWA News

Gwamnatin jihar Lagos ta bayar da umarni a bude ofisoshi da sauran hukumomin gwamnati daga ranar Litinin 04 ga watan Mayu.

A wata sanarwa ranar Juma’a, shugaban ma’aikata na jihar, Hakeem Muri-Okunola ya ce gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya amince da sake bude ofisoshin gwamnati a matsayin wata hanya ta aiwatar ta janye dokar kulle da aka saka a jihar.

Ya ce ma’aikata dake matakin albashi na 12 zuwa kasa za su cigaba da aiki daga gida a yayin da ake shawartar marasa lafiya da su kauracewa zuwa wurin aiki baki daya.

Ya kara da cewa ba a bawa jama’ar gari ko kuma ma’aikatan da aka hana zuwa aiki damar zuwa ma’aikatun ba.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...