Za a bude ofisoshin gwamnati ranar Litinin a Lagos – AREWA News

Gwamnatin jihar Lagos ta bayar da umarni a bude ofisoshi da sauran hukumomin gwamnati daga ranar Litinin 04 ga watan Mayu.

A wata sanarwa ranar Juma’a, shugaban ma’aikata na jihar, Hakeem Muri-Okunola ya ce gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya amince da sake bude ofisoshin gwamnati a matsayin wata hanya ta aiwatar ta janye dokar kulle da aka saka a jihar.

Ya ce ma’aikata dake matakin albashi na 12 zuwa kasa za su cigaba da aiki daga gida a yayin da ake shawartar marasa lafiya da su kauracewa zuwa wurin aiki baki daya.

Ya kara da cewa ba a bawa jama’ar gari ko kuma ma’aikatan da aka hana zuwa aiki damar zuwa ma’aikatun ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...