Zaɓaɓɓun Sanatoci Daga Arewa Sun Ce Dole Sai Shugaban Majalisar Dattawa Ya Fito Daga Yankin Su

Sanatocin da aka zaɓa daga yankin arewa sun dage cewa dole sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin arewacin kasarnan.

Wasu bayanai sun bayyana cewa zaɓaɓbun sanatocin 39 cikin 58 da suka fito daga jam’iyyu daban-daban sun gudanar da wani taro ranar Lahadi a Abuja inda suka cimma matsaya kan batun.

Wani sanata daga shiyar arewa maso yamma da yafi so kada a bayyana sunansa ya ce sanatoci da suka fito daga arewa sun dage sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin domin sakawa yankin kan goyon bayan takarar Bola Ahmad Tinubu a zaɓen da wuce.

Ya ce taron ya yanke matsayar tuntubar takwarorinsu da suka fito daga yankin kudu domin samun goyon bayansu.

More News

Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Ministan tsaro Badaru ya yaba wa gwamnan Zamfara saboda tallafa wa aikin soji a jihar

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da tallafa wa ayyukan soji a Jihar Zamfara.Ministan...