Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da wasu sanatocin jam’iyyar adawa ta PDP daga Jihar Kebbi waɗanda ake zargin suna shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar mai mulki ta APC.
Sanatocin da suka halarci ganawar a Fadar Shugaban Ƙasa ranar Juma’a sun haɗa da Sanata Adamu Aliero (Kebbi ta Tsakiya), Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi (Kebbi ta Arewa), da Sanata Garba Maidoki (Kebbi ta Kudu). Sun shiga ganawar ne tare da Shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.
Wasu jiga-jigan gwamnati da na jam’iyya da suka halarci ganawar sun haɗa da Ministan Tsare-tsaren Kasafin Kuɗi da Tattalin Arziƙi, Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi, Mohammed Nasir Idris da Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu Sokoto.
Wannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun yawaitar sauya sheƙa daga PDP zuwa APC. A baya-bayan nan, Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da wasu magoya bayansa sun sauya sheƙa zuwa APC, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a faɗin ƙasa.
Wasu na bayyana damuwa kan yuwuwar ƙasar na kaucewa tafarkin jam’iyyu da dama, sai dai fadar shugaban ƙasa ta musanta hakan.
Yunkurin Sauya Sheka: Shugaba Tinubu Ya Karɓi Baƙuncin Sanatocin PDP Daga Jihar Kebbi
