Yawan mutanen da suka mutu a ambaliyar ruwa a Libiya ya haura 11300

Yawan mutanen da suka mutu daga mummunan ambaliyar ruwan da ta samu birnin Derna dake gabashin kasar Libiya sun haura dubu 11300 a cewar Majalisar Dinkin Duniya(MDD) kamar yadda hukumar agaji ta Red Crescent dake kasar ta fada.

Karin wasu mutane 10100 ne suka bace a birnin.

A wasu wuraren dake gabashin kasar ta Libiya wajen birnin na Derna ambaliyar ta kashe akalla mutane 170.

Sanarwar ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana sa ran yawan mutanen zai cigaba da karuwa a yayin da ake cigaba da nema da kuma ceto jama’a.

Har ila yau ana cigaba da fuskantar karancin ruwan sha inda kawo yanzu yara 50 suka kamu da ciwo daga shan gurbataccen ruwa.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...