Yan sanda sun ceto wani malamin jami’a daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Nasarawa

Rundunar yan sandan jihar Nasarawa, ta ce jami’anta sun ceto wani malamin jami’ar jihar Nasarawa.

Malamin mai suna, Isaac Igbawua na fannin nazarin ƙananan kwayoyi halittu anyi garkuwa da shi ne ranar 27 ga watan Disamba.

Ramhan Nansel, mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce rundunar ta samu bayanai cewa wasu yan bindiga sun dira gida malamin dake Old Barracks a karamar hukumar Kokona.

Nansel ya ce yan sandan sun kuma samu bayanan sirri da suka taimaka musu wajen bin sahun yan bindiga zuwa wani daji dake Ogba a Nassarawan Eggon.

Ya ce hakan ya kai ga yin musayar wuta da yan bindigar a ranar 28 ga watan Disamba har ta kai ga an kubutar da malamin jami’ar ba tare da kwarzane ba.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...