Yan bindiga sun kashe mutane 21 a jihar Filato

Mutane akalla 21 aka bada rahoton an kashe a wani hari da yan bindiga suka kai kauyukan Baton da Rayogot a karamar hukumar Barikin Ladi ta jihar Plateau.

A wata sanarwa ranar Alhamis, Rwang Tengwong jami’in yada labarai na kasa na kungiyar Berom Youth Movement(BYM) ya ce mutane 10 ne suka samu raunuka a lokacin harin.

Ya ce yan bindigar sun kai farmakin kan kauyukan biyu da misalin karfe 1:26 na daren ranar Alhamis.

“Mutane 21 aka kashe a harin kan kauyukan biyu dake gudumar Heipang a Barikin Ladi” Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya jiwo Tengwong na fada.

Ya yi kira ga hukumomin gwamnati da su kawo dauki domin dakatar da kashe kashen da ake a jihar.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, Alfred Alabo ya ce rundunar za ta fitar da sanarwa nan gaba kadan kan harin.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...