‘Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6 a Anambra | BBC Hausa

Dakarun Nijeriya
Bayanan hoto,
Dakarun Nijeriya

Jami’an tsaro akalla shida ne suka hallaka a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.

Jami’an tsaron sun hada da sojojin ruwa uku da wasu yan bindiga suka harbe a garin Awkuzu da ke karamar hukumar Oyi.

Sai kuma jami’an ‘yan sanda uku da yan bindigar suka harbe a Neni da ke karamar hukumar Anaocha tare kuma da cinna wa motarsu wuta.

Al’amarin ya janyo zaman zulumi a jihar kuma ana rade radin cewa an sami wani gungun ‘yan bindiga da ke kai wa jami’an tsaro hari a jihar ta Anambra.

Rahotanni sun ce yan bindigar sun harbe sojin ruwan ne da karfe biyu na rana inda suka yi awon gaba da makamansu.

Jihar Anambra na cikin jihohin da aka hallaka jamian’yan sanda tare da kona caji ofis na yan sanda a watan Fabarerun daya gabata.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]