Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa Muhammad Buhari ta samu isa babban birnin Jihar Borno, wato, Maiduguri, a yau a cigaba da yakin neman zaben shugaban kasa na 2019.
Kamfanin Dillancin Labarai Na Najeriya, NAN ya ruwaito cewa jirgin shugaban kasar ya sauka da misalin karfe 10:30 na safe a bangaren sojan saman Najeriya na filin jirgin saman Maiduguri.
Buhari ya samu tarba da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshimhole, mashawarcin kasarnan kan harkar tsaro, Babagana Monguno da kuma karamin minista a ma’aikatar ayyuka, Mustapha Baba Shehuri.
Sauran manyan bakin da suka tarbi shugaban kasar,sun hada da gwamnan jihar, Kashim Shettima yan majalisun tarayya dana jiha da kuma sauran shugabannin jam’iyya.
Ana sa ran shugaban kasar zai yi wa magoya bayan jam’iyarsa jawabi dandalin Ramat dake birnin.