Yakin neman zaben: Buhari ya isa Maiduguri

Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa Muhammad Buhari ta samu isa babban birnin Jihar Borno, wato, Maiduguri, a yau a cigaba da yakin neman zaben shugaban kasa na 2019.

Kamfanin Dillancin Labarai Na Najeriya, NAN ya ruwaito cewa jirgin shugaban kasar ya sauka da misalin karfe 10:30 na safe a bangaren sojan saman Najeriya na filin jirgin saman Maiduguri.

Buhari ya samu tarba da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshimhole, mashawarcin kasarnan kan harkar tsaro, Babagana Monguno da kuma karamin minista a ma’aikatar ayyuka, Mustapha Baba Shehuri.

Sauran manyan bakin da suka tarbi shugaban kasar,sun hada da gwamnan jihar, Kashim Shettima yan majalisun tarayya dana jiha da kuma sauran shugabannin jam’iyya.

Ana sa ran shugaban kasar zai yi wa magoya bayan jam’iyarsa jawabi dandalin Ramat dake birnin.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...