Rundunar ‘yan sandan jihar ta Katsina, ta ce yan bindiga kimanin 300 ne suka far wa kauyuka uku na Kirtawa da Kinfau da Zamfarawan Madogara da ke yankunan kananan hukumomin Batsari da Safana.
A wata sanarwa, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Gambo Isah ya ce hare-haren da aka kai ranar Asabar, sun yi sandiyyar mutuwar mutum 10, inda kuma aka jikkata mutum biyar.
DSP Gambo Isah ya kuma ce ‘yan bindigar sun rika harbin kan mai uwa da wabi inda suka tarwatsa mutanen kauyen.
Sanarwar ta kara da cewa maharan sun cinna wa ababan hawa wuta,bayan sun kora shanun da ba a san adadinsu ba.
Wani wanda harin ya rutsa da shi a kauyen Zamfarawan Madogara ya bayyana wa Sani Aliyu yadda lamarin ya auku.
Wannan bawan Allah ya kara da kokawa dangane da yadda ‘yan bindiga ke satar mata a duk lokacin da suka kai hare-hare kauyukan nasu.