Yadda ‘yan bindiga 300 suka far wa kauyukan Katsina | BBC Hausa

Soldiers
Image caption

Jami’an tsaro sun sha alwashin kawo karshen matsalar tsaro

Rundunar ‘yan sandan jihar ta Katsina, ta ce yan bindiga kimanin 300 ne suka far wa kauyuka uku na Kirtawa da Kinfau da Zamfarawan Madogara da ke yankunan kananan hukumomin Batsari da Safana.

A wata sanarwa, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Gambo Isah ya ce hare-haren da aka kai ranar Asabar, sun yi sandiyyar mutuwar mutum 10, inda kuma aka jikkata mutum biyar.

DSP Gambo Isah ya kuma ce ‘yan bindigar sun rika harbin kan mai uwa da wabi inda suka tarwatsa mutanen kauyen.

Sanarwar ta kara da cewa maharan sun cinna wa ababan hawa wuta,bayan sun kora shanun da ba a san adadinsu ba.

Wani wanda harin ya rutsa da shi a kauyen Zamfarawan Madogara ya bayyana wa Sani Aliyu yadda lamarin ya auku.

Yadda aka far wa kauyukanmu

Wannan bawan Allah ya kara da kokawa dangane da yadda ‘yan bindiga ke satar mata a duk lokacin da suka kai hare-hare kauyukan nasu.

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...