Yadda ‘wani ya kashe abokinsa kan N500 a Kano’ | BBC Hausa

Habu Sani

Bayanan hoto,
Kwamishina Habu Sanine ya tabbatar wa da BBC labarin

Rundunar ƴan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta tabbatar da mutuwar wani matashi mai shekara 22 da ake zargin wani abokinsa da kashe shi sakamakon wani saɓani da ya shiga tsakaninsu.

Yayin da yake tabbatar wa da BBC faruwar al’amarin, kwamishinan Æ´an sandan jihar Habu Sani, ya ce wanda ake zargi da kashe Sani Ibrahim ya yi hakan ne a kan Naira 500, ta hanyar caka masa wuka a Æ™irji, kuma hakan ya yi sanadin mutuwarsa.

To sai dai wani mazaunin unguwar da abun ya faru a kan idonsa Basiru Ahmad, ya ce daÆ™iÆ™a kaÉ—an kafin faruwar al’amarin, matasan biyu sun tsaya a wajensa har ya yi musu nasihar su zauna lafiya da junansu sannan suka tafi.

“Sun zo wajena mintina kaÉ—an kafin faruwar al’amarin, don mun gaisa da su har na yi musu fada cewa su zauna lafiya, babu hayaniya suna cewa da ni ai babu komai.

”Daga nan sai shi Sani Ibrahim ya je fitsari, to da yake gurin da duhu ban iya gane waye ya je inda yake fitsarin yake masa magana ba, sai na ga wani ma ya je kansa, daga nan sai jin Æ™ararsa muka yi su kuma waÉ—ancan sun gudu”, a cewar Basiru Ahmad.

Wani daga cikin abokan mamacin Sani Alhassan ya ce suna gefe suna hira bayan dawowarsa daga sana’arsa ta tuÆ™a babur É—in a-dai-dai-ta sahu, suka ga ana taruwa a inda aka kashe matashin, shi ne suka je suka tarar da Sanin a kwance ya dafe Æ™irjinsa, yana faÉ—in sunan wanda ake zargi da kashe shi.

Me iyayen Sani ke cewa?

Zainab Isma’il ita ce mahaifiyar Sani, a hirarta da BBC ta nemi hukuma da ta bi mata hakkin É—anta, wanda ta ce maraya ne kuma shi ke É—awainiya da ita.

”Gani na da shi na Æ™arshe shi ne lokacin da ya shigo don ya gaishe ni saboda ba ni da lafiya, daga nan sai ya cetun da bacci nake bari ya je ya dawo.

”Can kuma sai na ji ana sallama ana cewa wai in zo ga Sani can an caka masa wuÆ™a a Æ™irji, shi ne na ce ba zan je ba su kawo min shi kawai don duk Æ™irji makasa ne, kashe shi dama suka yi niyar yi, inji mahaifiyar ta Sani.

Malama Zainab ta ci ga da cewa: ”Shi kadai nake da shi kuma shi ke taimaka min, ya kan je Fatakwal yana harkar gwangwan É—insa, kuma da tuni ya tafi amma saboda rashin lafiyar da nake shi ya sa bai tafi ba ya ce sai na ji sauÆ™i.

“Dama suna yawan tsokanar sa, amma duk da na hana shi daka ta tasu su yi fada amma sai sun takale shi,” in ji mahaifiyarsa Sani.

Bayanan hoto,
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ana binciken lamarin a sashen binciken manyan laifuka

Tuni dai kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano Habu Sani ya tabbatar da kama wanda ake zargin, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike tare da mayar da batun sashen binciken manyan laifuka na rundunar yan sanda jihar.

A baya-bayan nan ma an samu rahoton yadda wani matashi mai suna Ashiru Danrimi mai shekara 22 da zargin ya kashe kansa, saboda budurwarsa ta zabi auren wani daban ba shi ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...