Wata mata ta cinna wa gidan mijinta wuta saboda ya ƙi ya sake ta

Hukumomi sun kama wata amarya ‘yar shekara 20 mai suna Amina Hassan daga karamar hukumar Mubi ta Arewa a jihar Adamawa bisa laifin cinna wa gidan mijinta wuta.

Amina ta ɗauki wannan matakin ne saboda kin rubuta mata takardar saki.

An ce ma’auratan sun kulla yarjejeniya kafin aurensu.

A cewar wasu rahotanni, Amina ta sanar da iyayenta cewa ba ta da sha’awar yin wannan auren kwanaki kadan kafin ɗaurin auren.

Duk da haka, iyayenta sun dage cewa dole ne a yi bikin aure saboda sun riga sun raba katunan gayyata.

Bayan an daura auren ne ta nemi taimakon wani boka don ya sa mijinta ya tsane ta ya sake ta.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...