Wani riƙaƙƙen mai laifi da ya tsere daga gidan yarin Jos ya sake faɗawa hannun jami’an tsaro

Sojojin shiya ta ɗaya na rundunar haɗin gwiwa ta Operation UDO KA II dake yakin kudu maso gabas tare da haɗin gwiwar jami’an hukumar tsaro ta DSS na jihar Enugu sun kai wani samame maboyar yan ta’addar IPOB a jihar

Maboyar na kauyen Ugbakwa dake karamar hukumar Nkanu East ta jihar Enugu.

A yayin farmaki jami’an sun samu nasarar kama, Chimezie Chukwu wanda aka fi sani da Biggi da ya tsere daga gidan yarin Jos.

Biggi ya kasance fitaccen mai safarar bindigogi, kwayoyi baya da ficen da yayi a fashi da makami.

Kayan da aka samu a wurinsa sun haɗa da wayoyin hannu guda 6, baturan waya uku, na’urar POS ta Moniepoint, katin ATM, fakiti biyu da ake zargin tabar wiwi ce.

Naira dubu ɗari bakwai da ɗari biyu da tamanin aka samu a wurinsa.

A yanzu haka yana hannun jami’an hukumar tsaro ta DSS domin cigaba da bincike.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...