Wani direba ya kashe jami’in hukumar FRSC a Lagos

Wani jami’in hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa FRSC ya gamu da ajalinsa bayan da wani direba ya matse shi a tsakanin motoci.

Shedun gani sun ce an matse jami’in na FRSC ne a tsakanin motoci inda kansa ya fashe ya yi ta zubar da jini.

Bisi Kazeem mai magana da yawun hukumar FRSC ya ce lamarin ya faru ne a yankin Orile-Iganmu a jihar Lagos ranar Asabar.

Sai dai Kazeem ga gaza bayyana ko an ankama direban motar da ya aikata haka.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]