Tsohon gwamnan jihar Kaduna Alhaji Mukhtar Ramalan Yero ya fice daga jam’iyyar PDP.
Malam Yero ya mika takardar murabus dinsa ga jam’iyyar PDP a yau a wata takarda da ya sanyawa hannu.
Wasikar ta ce, “Tare da godiya ga Allah Madaukakin Sarki, na rubuto ne domin in mika sakon gaisuwata tare da sanar da ku matakin da na dauka na ficewa daga jam’iyyar PDP.
“Saboda haka, na gabatar da murabus É—ina a matsayin mamba na Jamiyyar PDP, wadda za ta fara aiki daga ranar 30 ga Satumba, 2023.”
Tsohon gwamnan dai bai bayyana dalilin mika takardar murabus din ba.