Shugaban Najeriya Bola Tinubu, a ranar Litinin, ya gana da shugabannin kungiyar ma’aikatan lafiya, JOHESU.
Kungiyar ta kwashe sama da mako guda tana yajin aiki, inda ta janye mambobinta daga asibitocin gwamnati a fadin kasar.
A ganawar tasu ta ranar Litinin, Mista Tinubu ya bukaci kungiyar JOHESU da ta janye yajin aikin ta kuma baiwa mambobinta, ma’aikatan lafiya da likitoci hakuri da su koma bakin aiki.
Bayanin taron na kunshe ne a cikin sanarwar da Abiodun Oladunjoye, daraktan yada labarai na fadar gwamnatin jihar ya fitar.
“Bangaren lafiya bangare daya ne da ke da muhimmanci ga bil’adama. Za mu warware dukkan matsalolin,” in ji Mista Tinubu a wajen taron.