Tinubu ya haɗu da Okonjo-Iweala, Shugabar WTO

Shugaba Bola Tinubu yana ganawa da Ngozi Okonjo-Iweala, Darakta Janar ta kungiyar kasuwanci ta duniya WTO a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Okonjo-Iweala ta isa fadar shugaban kasa ta Villa tare da tsohon karamin ministan lafiya, Dr. Ali Pate da misalin karfe 2:50 na yammacin ranar Talata.

Kawo yanzu dai ba a san makasudin taron ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Ku tuna cewa Okonjo-Iweala a farkon watan Yuni ta gana da Tinubu a lokacin da dukkansu suka halarci taron shugabannin da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa.

Okonjo-Iweala ita ce ministar kudi a zamanin gwamnatin tsohon shugaban kasa Good luck Jonathan.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]