Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC Abdulrashid Bawa

Shugaba Bola Tinubu ya amince da dakatar da shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, AbdulRasheed Bawa daga aiki.

Ya yi haka ne domin ba da damar gudanar da bincike mai inganci a kan yadda yake gudanar da ayyukansa a lokacin da yake kan mulki.

A cewar sanarwar da Daraktan Yada Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey ya fitar, matakin ya biyo bayan zarge-zargen “mai nauyi” na cin zarafin ofishin da aka yi masa.

“An umurci Mista Bawa da ya gaggauta mika al’amuran ofishinsa ga Daraktan Ayyuka a Hukumar, wanda zai kula da harkokin ofishin Shugaban Hukumar har zuwa karshen binciken,” in ji sanarwar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...