Sojojin Najeriya sun kashe babban kwamandan Iswap

Sojojin Najeriya sun ce sun kashe ɗaya cikin manyan kwamandojin Iswap da wasu mayaƙa a wani farmaki a arewa maso gabashi.

Sojojin sun ce sun kashe kwamandan mai suna Abubakar Danbuduma da mayaƙa 19.

Rundunar sojin ta ce dakarunta sun kai harin ne a yankin Tafkin Chadi ta hanyar amfani da jiragen yaƙi.

Abu ne mai wahala a iya tantance gaskiyar labarin. Amma wannan na zuwa a yayin da mayaƙan Iswap ke karɓe ikon wasu ƙauyuka tana tilasta wa mutane biyan haraji

More from this stream

Recomended