Dakarun sojojin Najeriya a wani samame daban-daban da suka kai a jihohin Zamfara da Katsina sun kashe ‘yan ta’adda 11.
A garin Zamafara, an kai samame maboyar wani shugaban ‘yan ta’adda, Hassan Yantagwaye, a karamar hukumar Tsafe, wanda ya yi sanadin fafatawa da ‘yan ta’addan guda biyu a harin.
Hakan na kunshe ne a wani sako da rundunar sojin Najeriya ta fitar a ranar Litinin.
A cewar saƙon, “Dakarun Sojojin Najeriya da aka tura domin Yaki da Ta’addanci a Jihohin Katsina da Zamfara, a wani jerin hare-hare na hadin gwiwa sun kai farmaki a yankunan ‘yan ta’adda wanda ya yi sanadin kawar da dimbin ‘yan ta’adda.
“A wani samame da suka kai jihar Zamfara, a ranar 29 ga Maris, 2024, sojoji sun yi nasarar kai samame a kogon wani fitaccen sarkin ‘yan ta’adda, Hassan Yantagwaye, a karamar hukumar Tsafe.
“A yayin farmakin, sojoji sun fatattaki ‘yan ta’addan a wani artabu da suka yi da su, inda suka kashe uku daga cikinsu tare da kwato tarin makamai da alburusai. Sojojin sun kuma lalata sansanonin ‘yan ta’addan.”