Sojoji sun kashe kwamandojin ƴan ta’adda a Najeriya

Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta ce bangarenta na rundunar Operation Hadin Kai a ranar 10 ga watan Janairu ya kawar da wasu manyan kwamandojin ISWAP da ‘yan ta’adda uku a Borno.

Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaron, Maj.-Gen. Edward Baba, ne ya bayar da wannan tabbacin a cikin rahoton mako-mako na ayyukan rundunar a ranar Juma’a a Abuja.

Mista Buba ya ce kwamandojin uku an bayyana sunayensu kamar haka: Abou Maimuna, Abou Zahra da Kwamanda Saleh tare da kwamandansu a cikin kwalekwale.

Har yanzu dai jami’an tsaron Najeriya na ta fama ba dare ba rana wajen ganin sun kawar da ta’addanci a fadin ƙasar amma abin ya ci tura.

More News

Za a rataye wanda ya ɗaba wa wani wuƙa har lahira

An yanke wani mutum mai suna Hamza Mohammed  hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan da ya daba wa wani mutum wuka har lahira a...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Mahaifi ya fille kan ɗiyarsa don yin asiri

Jami’an tsaro na jihar Edo sun kama wani mutum mai suna Emmanuel Ovwarueso bisa zarginsa da fille kan diyarsa bisa zarginta da laifin kashe...