Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno ta bi ta kan wani abin fashewa da ake zargin ‘yan ta’addar ISWAP ne suka dasa.

Sahihan majiyoyin leken asiri na soji sun shaida cewa lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 17 ga Afrilu.

Kakakin runduna ta 7, Laftanar Kanal Ajemusu Jingina, ya ce, “Ba zan yi magana a kan lamarin ba, domin wurin yana karkashin ikon rundunar hadin gwiwa ta Multi-National Joint Task Force, wadda ke da hedikwata a Ndjamena, Jamhuriyar Chadi.”

Jihar Borno dai na daga cikin jihohin da ke fama fa tashin hankali ƴan Boko Haram.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...