Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno ta bi ta kan wani abin fashewa da ake zargin ‘yan ta’addar ISWAP ne suka dasa.

Sahihan majiyoyin leken asiri na soji sun shaida cewa lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 17 ga Afrilu.

Kakakin runduna ta 7, Laftanar Kanal Ajemusu Jingina, ya ce, “Ba zan yi magana a kan lamarin ba, domin wurin yana karkashin ikon rundunar hadin gwiwa ta Multi-National Joint Task Force, wadda ke da hedikwata a Ndjamena, Jamhuriyar Chadi.”

Jihar Borno dai na daga cikin jihohin da ke fama fa tashin hankali ƴan Boko Haram.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...