Sojoji sun kama mayakan IPOB 5 a yayin farmaki kan maboyar su

Rundunar sojan Najeriya tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro sun kama wasu mutane 5 da ake zargin su da kasancewa mambobin kungiyar Eastern Security Networ(ESN)

ESN bangare dake fada da makamai na kungiyar IPOB dake fafutukar kafa kasar Biafra.

Mutanen dai sun fada hannun jami’an tsaro a ranar Litinin a dajin Orsomoghu da ya hada jihohin Imo da Anambra.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Talata mai magana da yawun rundunar sojan Najeriya, Onyeama Okechukwu ya ce an kama mutanen ne a yayin wani samame da aka kai kan masu ta tabbatar da dokar hana fita ranar Litinin a yankin kudu maso gabas.

Sanarwar ta ce duk da cewa mutanen sun tayar da bama-bamai tare da bude wuta jaruman sojojin sun samu nasarar kama wasu a yayin da wasu suka tsere da raunin harbin bindiga.

A karshe sanarwar ta bayyana cewa sojoji biyar da yan sanda biyu ne suka samu raunuka sanadiyar fashewar bam a yayin farmakin.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...