Sojoji Sun Ceto Ma’aikatan Agaji Biyu Daga Hannun ISWAP A Borno

Sojojin rundunar Operation Desert Sanity 2 sun samu nasarar ceto biyu daga cikin ma’aikata uku na kungiyar agaji ta Family Health International (FHI360) da mayakan kungiyar ISWAP suka sace a Borno.

Mayakan na ISWAP sun sace ma’aikatan agajin ne tare da wasu jami’an tsaro biyu a wani hari da suka kai masaukin su dake Gamborun Ngala a ranar 26 ga watan Afrilu.

Wata majiya ta bayyana cewa an É—auke mutanen zuwa wani wuri da ba sani ba.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan rikicin dake faruwa a yankin tafkin Chadi an ceto ma’aikatan agajin ne a yayin musayar wuta da aka yi tsakanin sojoji da mayakan ISWAP a wajejen garin Banki dake karamar hukumar Bama.

Zagazola ya ce a yayin musayar wutar ma’aikatan agajin sun diro daga motar yan ta’addar inda suka yi gaggawar bayyana kansu ga sojojin.

Jami’an tsaron biyu da kuma É—aya daga cikin ma’aikatan agajin sun tsere cikin daji kuma kawo yanzu ba a gansu ba.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...