Shugaban majalisar dokokin jihar Edo ya kamu da Coronavirus – AREWA News

Shugaban majalisar dokokin jihar Edo, Frank Okiye ya kamu da cutar Coronavirus.

Mataimakin gwamnan jihar,Philip Shaibu shi ne ya sanar da haka yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a babban birnin jihar ranar Laraba.

Ya ce tun da farko kakakin majalisar shi ne mutumin da gwamnatin jihar take nufi ya kamu da cutar a sanarwar da ta fitar na samun bullar cutar a jihar.

Tun lokacin da ya dawo daga kasar Birtaniya, shugaban majalisar ya killace kansa.

More from this stream

Recomended